Yadda aka Gudanar da Addu’ar sadakar Uku da bakwai na Nura Mustapha waye ba’aga Adam a zango da Naziru sarkin waka awajan ba
Mutane sunfara cece kuce akan rashin zuwan jarumi Adam a zango da Naziru sarkin waka wajan Ta’aziyar Marigayi Nura Mustapha waye.
Idan mai karatu bai mantaba dai kasa da makonni biyu kenan da Allah ya karbi rayuwar marigayi Nura Mustapha waye a gidansa, wanda rasuwarsa ta matukar tayar da hankalin mutane.
Domin rasuwar tashi tazo da bazata kasancewar ya kwanta lafiya kalau baby wani rashin lafiya a taredashi inda har wayewar safiyar ranar lahadi dazai rasu yatashi yaje masallaci yayi sallah asuba yadawo gida bayan ya kammala karatunsa yadan sake kwantawa ashe kwanciyar da bata tashi ba kenan.
Saidai zamu iya cewa rashin ganin fusjar jarumi Adam a zango da Naziru Sarkin waka hakan bazai zama wani abun magana ba, domin akwai jaruman da dayawa ba’aga fuskarsu awajan mutuwar marigayin ba.
Kamar yadda Lawan Ahmad ya bayyana cewar akwai wanda suka kirasu ta waya domin yimusu Ta’aziya haka zalika akwai wanda suka yimusu “Text Message” ta gaisuwa wanda basai sun fadi sunayensu ba.
Ga video
Allah ubangiji yaji kansa da Rahama Amin.
Kucigaba da bibiyar shafinmu maisuna Arewajoint domin samun labarai cikin sauki akoda yaushe mungode.