‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗalibin Kwalejin Ilimi Ta Tarayya Dake Katsina A Yawon Sallah

Daga cikin waɗanda ‘yan bindiga-daɗi suka kai wa farmaki a yayin dawowa daga yawon Sallah a cikin birnin Katsina, hada ɗalibin Kwalejin Ilimi Ta Tarayya da ke Katsina (FCE Katsina), ɗalibin mai suna Anass Adamu.

Shi ne wanda ya rasa r@nsa yayin gudun tsira daga wajen ‘yan bindiga-daɗi a hanyarsu ta komawa Ƙaramar Hukumar Jibia.

Ɗalibin mai suna Anass Adamu ya kammala karatunsa wanda yake a sashen SOS a lambar karatu ta (41Series), wanda har yanzu ba ma a fara ba ‘yan lambar karatunsu result ba, ɗalibin dai yana zaune tare da mahaifansa a Ƙaramar Hukumar Jibia ta jihar Katsina.

Allah ubangiji yaji kansa da Rahama Amin.
Daga Zaharaddeen Gandu

Kucigaba da bibiyar shafinmu maisuna Arewajoint.com domin samun labarai cikin sauki akoda yaushe mungode.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button